Ƴan banga sun kashe ƴan Boko Haram yayin da suka je satar amfanin gona

Ƙungiyar yan sa kai a arewa maso gabashin Najeriya ta kashe ƴan Boko Haram uku da kama ɗaya a yayin da ƴan Boko Haram ɗin suka je satar amfanin gona a kan hanyar Maiduguri zuwa Damaturu.

Hoto: hutudole

BBC ta ce Kafar PRNigeria ta ruwaito cewa ƴan Boko Haram sun kai hari ga wasu manoma tare da satar amfanin gonarsu inda ƴan sa kan suka yi bata-ka-shi da su.

Wani wanda ya gane ma idonsa lamarin ya ce mayaƙan sun kashe manoma biyu da kuma raunata wani mutum guda.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram