Obasanjo na son ƴan Najeriya su rika amfani da makamashin da ba ya gurɓata muhalli

Tsohon shugaban Ƙasar Najeriya Olusegun Obasanjo ya buƙaci ƴan ƙasar su rungumi tabi’ar amfani da makamashi wanda ba ya gurbata muhalli domin a samu ƙasa mai tsafa.

Obasanjo ya yi kiran ne ranar Juma’a nan a yayin da yake ƙaddamar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana mai ƙarfin 2MW a ɗakin Karatun da ya gina da ke birnin Abeokuta na jihar Ogun.

BBC ta ce, Jaridar ThisDay ta ambato tsohon shugaban ƙasar yana cewa amfani da makamashi mai aiki da hasken rana “yana da arha kuma yana da kyau ga muhalli.”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram