An Sanya Ranar Buɗe Layukan Waya A Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya ce ranar Talata nan mai zuwa za a bude layukan wayar salula a fadin jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a yayin zaɓen shugabannin jam’iyyar APC reshen jihar Zamfara ranar Asabar ɗinnan.

In za a iya tunawa dai a farkon watan Satumba ne aka katse layukan a wani mataki na daƙile hare-haren ƴan bindiga da masu satar mutane.

Sai dai a kwanakin baya an bude layukan wayar salula da intanet da aka katse a Gusau, babban birnin jihar.

Matawalle ya kara da cewa za a sake buɗe kasuwannin da aka rufe sakamakon matsalar tsaro.

“Bayanan da muka samu sun nuna cewa an samu raguwar matsalolin tsaro a yankunan jihar nan, kuma nan da Litinin ko Talata za mu sake bude layukan wayoyin salula, kowa da kowa zai samu damar yin waya,” in ji gwamnan.

#BBC

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram