An Samu Ƙarin Mutane 23 Masu Ɗauke Da Cutar Korona A Katsina.

Hukumar ɗakile cututtuka masu yaɗuwa a Najeriya ta ce an samu ƙarin mutane 110 da suka kamu da cutar korona a Najeriya.

Alƙalumman sun nuna mutum 27 suka kamu da cutar a jihar Imo sai a jihar Katsina da aka samu mutum 23 a ranar Lahadi.

A jihar Rivers an samu mutum 20, sai jihar Ondo mai mutum 11. A Kaduna ƙarin mutum tara suka kamu da cutar.

Yanzu jimillar mutum 214,092 cutar ta shafa a Najeriya amma 207,254 sun warke yayin da cutar ta kashe mutum 2,976 a Najeriya.

#BBC

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram