Buhari Ya Gana Da Tambuwal Game Da Matsalar Tsaro A Sokoto

A rahoton da muka samu Shugaba Muhammadu Buhari yana kan ganawa da Gwamna Aminu Tambuwal na jahar Sokoto dangane da sha’anin tsaro a jahar.

Mai taimaka ma shugaban ƙasar kan kafafen sada zumunta na zamani, Bashir Ahmed ne ya sanar da haka a shafinsa na Facebook.

Bashir Ahmed ya ce shugaba Buhari na ganawa da Tambuwal ɗin ne da daddaren nan a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Sokoto dai ta shiga cikin jerin jahohin Arewa da ke fuskantar matsalar aikace-aikacen ƴan bindiga da ke faruwa a yankin Arewacin ƙasar.

Ko a satin da ya gabata ƴan ta’adda sun tare mota ɗauke da matafiya inda suka ƙona matafiyan kimanin mutum 42 da ma wasu hare-haren da suka kai daga baya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram