Matsalar Tsaro: Zanga-zanga A Jahar Kano: Ana Ci Gaba Da Gasa Ma Buhari Aya A Hannu

An ci gaba da yin zanga-zanga bisa ga nuna kin jinin rashin tsaro a Arewacin Najeriya.

Martaba FM ta ruwaito, yau ma a jahar Kano wasu mutane sun fito domin yin zanga-zangar kuma da yawansu matasa ne.

Hotuna: Abba Adam Isah

A ƴan kwanakin nan dai kusan jahohin da ke Arewa kalan ne ba a samu waɗanda suka fito zanga-zanga ba saboda matsar tsaro da ke addabar yanki.

Ko a jiya ma an so a yi zanga-zangar a Katsina sai dai jami’an tsaro sun shawo kan lamarin kafin ya yi ƙamari.

A kano dai wata matashiya mai suna Zainab ta shirya zanga-zangar lumana a kwanan nan sai dai daga bisani ta nisanta kanta daga zanga-zangar bayan da DSS suka gayyace ta ofishinsu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram