Yanzu-Yanzu: Yan bindiga Sun yi Garkuwa da Basaraken Gargajiya A Filato

Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da Charles Mato Dakat, babban basaraken garin Gindiri da ke karamar hukumar Mangu a jihar Filato.

Jaridar Daily Trsut ta ruwaito cewa an yi garkuwa da basaraken ne bayan an yi ta harbe-harbe a gidansa da sanyin safiyar Lahadi.

Manjo Ishaku Takwa, kakakin rundunar ‘Operation Safe Haven’ (OPSH), da ke aikin tabbatar da zaman lafiya a jihar, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce an tura jami’an sojoji zuwa yankin kuma suna nan ana bin sahun masu garkuwa da mutane.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram