In Ka Rasa Ranka A Yayin Kare Kanka Daga Ƴan ta’adda Ka Yi Jihadi – Masari

Gwamnan jahar Katsina Aminu Bello Masari, ya sake jaddada kiransa ga al’umma musamman jama’ar jahar ta Katsina da su tashi tsaye wajen neman makaman da za su kare kawunansu a yayin da ƴan ta’adda suka kawo ma su hari.

Gwamnan ya ce bai yiwuwa a zo gabanka a wulaƙantaka a ci mutuncin ƴaƴanka da matanka kuma ka sa ido ka kyale.

Masari ya ce ai ba zata saɓu ba mutanen banza su ɗauki makamai amma a ce mutumin kirki ba zai riƙe makami ya kare kanshi ba.

Masari ya ce yana da kyau mutane su dage da maida bugu, ya ce a irin wannan in mutum ya rasa ranshi to yayi jihadi

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram