Ƴan bindiga Sun Kai Hari A Bunguɗu, Sun Yi Awon Gaba Da Mutane Da Dama

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan fashin dajin ne, sun kai hari kauyen Gada da ke karamar hukumar Bungudu tare da kashe Hakimin yankin.

‘Yan bindigar sun kuma yi awon gaba da wasu mutanen da ba a tantance adadinsu ba

A daren ranar Talata ne suka mamaye yankin da manyan makamai tare da yi wa jama’a barazana

Kwamishinan yada labarai na jihar Zamfara Ibrahim Dosara ya tabbatar da faruwar lamarin

Ya ce gwamnatin jihar na aiki tukuru domin ganin ta kawar da irin wadannan miyagun ayyuka

Ibrahim Dosara a madadin gwamnati ya jajantawa al’ummar da abin ya shafa, da iyalan sarkin gargajiya da iyalan wadanda aka yi garkuwa da su.

Al’ummomin da ke karkashin karamar hukumar Bungudu a ‘yan kwanakin nan sun fuskanci hare-haren ‘yan bindiga da ya kai ga kauracewar mazauna yankin da dama.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram