Albishirinku Ƴan Najeriya: Sabon Minstan Wutar Lantarki Ya Ce Ba Da Jimawa Ba Zasu Samar Da Wutar Lantarki Mai Ƙarfin Megawatt Dubu 25

Ma’aikatar kula da wutar lantaki ta tarayyar Najeriya ta bayyana shirin da take na samar da wutar lantarki mai karfin megawatt dubu 25 nan ba da jimawa ba.

A cewar sabon ministan ma’aikatar, Injiniya Abubakar Aliyu, ma’aikatar ta samar da na’urori da sauran kayayyakin aiki da dama a karkashin shirin shugaban kasa na bunkasa hasken wutar lantarki da nufin inganta lantarkin da ma sana’o’in da ke da alaka da lantarkin.

Aliyu ya bayyana hakan ne a Katsina a sa’ilin da ya kai ziyarar duba ayyukan tasoshin wutar lantarki a jihar ciki har da aikin samar da lantarki ta hanyar iska da ke Lambar Rimi a yankin karamar hukumar Charanchi.

Aikin na Lambar Rimi wanda aka bayar da kwangilarsa tun a watan Yunin 2009 na da nufin samar da megawatt 10 na wutar lantarki domin amfanin jihar kuma an sa ran kammala shi ne tun a wancan lokaci a cikin watanni 24.

Rahoton da muka samu ya nuna cewa dan kwangila na farko ya soma aikin ne a shekarar 2010 kuma bayan hakan sai aka sace injiniyan da ke kula da aikin a lokacin da aikin ya yi nisa, abin da ake ganin shi ne ya soma haddasa tsaikon kammaluwar aikin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram