Da Ɗumi-ɗumi: Allah Ya Yi Ma Babban Malami Sheikh Ahmad Bamba Rasuwa

Allah ya yi ma fitataccen malamin nan na Kano, Sheikh Ahmad Muhammad Ibrahim Bamba rasuwa.

Malamin wanda aka fi sani da Ƙala Haddasana ya rasu a yau juma’a bayan gajeruwar jinya.

Babban malamin ya yi fice a fagen karatuttukan Hadisi a masallacinsa mai suna Darul Hadis.

Za a yi jana’izar Dr. Ahmad bayan juma a masallacin na Darul Hadis da ke Kano.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram