Da ɗuminsa: Buhari Ya Ɗage Haramcin Yin Twitter, Baya Shafe Tsawon Watanni 7

Bayan shafe tsawon watanni bakwa, Gwamnatin Tarayya ta ɗage dokar hana Twitter a Najeriya, bayan amincewa da Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya yi.

Daraktan Kwamitin Tattaunawa da Twitter,kuma Shugaban Hukumar Kula da cigaban Fasaha ta Najeriya Kashifu Inuwa Abdullahi ya sanar da hakan.

Abdullahi a cikin sanarwar da ya fitar a Abuja, yace an bada amincewar, biyo bayan wata sanarwa da Ministan Sadarwa Prof Isa Ali Pantami ya aikewa Buhari.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram