Mai magana da Yawun Jigon Jamiyyar APC ya bayyana haka, yana mai cewa, tuntuben harshe ne da Tsohon Gwamnan jihar Lagos yayi, inda yace akwai bukatar sake sabunta bayanan katin zaben.
Asiwaju Tinubu ya kuma yabawa kokarin da Hukumar INEC ke yi wajen tabbatar da an shiryawa jam’iyyun siyasa zabe na gari.
karshe Tinubu ya yi kira da babbar murya ga mata da sauran Jama’a da su rika fita su na kada kuru’un su da zaran lokacin zaben yayi.
Hukumar zaben, ta maida martani game da kalaman na Bola Tinubu, Inda tace sam basu tashi aiki ba, kuma za’a yi duk wasu zaben dake tafe da katunan.