Ba Zan Sake Komawa Jam’iyyar PDP Ba – In Ji Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo ya sake jaddada kudurinsa na kaurace wa siyasar bangaranci, ya kuma ci gaba da zama dattijon dan siyasa.

Ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin wasu shugabannin jam’iyyar PDP da suka kai masa ziyara a dakin karatu na shugaban kasa da ke Abeokuta.

Tawagar wacce shugaban jam’iyyar na kasa, Iyorchia Ayu ya jagoranta, ta hada da dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar PDP a 2019 da tsohon gwamnan jihar Anambra, Peter Obi; Sule Lamido na Jihar Jigawa; Olusegun Mimiko, Liyel Imoke, Donald Duke da dai sauransu.

Tsohon shugaban kasar ya yaba da wannan ziyara inda ya ce duk wanda ke son shawararsa a kodayaushe zai kasance a bude domin tuntubar shi domin amfanin Najeriya.

Inda ya ce amma shi babu abunda zai sake mayar da shi cikin jam’iyya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram