Buhari Ba Ya Goyon Bayan Cire tTallafin Man Fetur

Ƙaramin Ministan Man Fetur Timipre Sylva yace Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari yace Shugaban Ƙasa baya goyon bayan cire tallafin Man Fetur.

Sylva ya bayyana haka a lokacin da ya bayyana a shirin Newsnight na gidan Talabijin na Channels.

“Zan gaya maku a wannan lokacin cewa, cire tallafin mai gaba ɗaya bashi ne ke gaban mu ba.

“Shugaban Ƙasar Najeriya baya goyon bayan cire tallafin man fetur a wannan lokacin,” inji shi.

Ministan ya bayyana cewar daga cikin dalilan da suka sanya Gwamnatin Tarayya bata tunanin cire tallafin man fetur saboda abinda zai haifar ga ƴan Najeriya.

“Yace ” wannan abune dake buƙatar yin aiki tsakanin Gwamnatin Tarayya da Jahohi, saboda abinda ya shafi ƙasa ne. Muna aiki da Gwamnoni a halin yanzu.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram