Da Ɗumi-Ɗumi: Abdulmalik Tanko Ya Musanta Zargin Da Ake Masa Na Kashe Hanifa Abubakar

Mutumin nan mai suna Abdulmalik Tanko ya musanta zargin da ake masa na kisan da kuma garkuwa Hanifa Abubakar ƴar shekara 5.

A ranar Litin ɗin nan ne aka sake kai Tanko da mutane biyun da ake zargin sun aiakata laifin tare, Hashimu Isyaku da Fatima Jibrin a gaban Babbar Kotun jahar Kano ƙarƙashin jagorancin Alƙali Usman Na-Abba.

Da farko dai an karanto masu tuhume-tuhumen da ake yi masu, saidai dukkansu sun musanta.

Da aka tambayi Tanko yayi garkuwa da kuma kashe Hanifa? Sai ya ce, “ban aikataba.”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram