Da Ɗumi-Ɗumi: Kwankwaso Ya Fice Daga PDP, Ya Kafa Sabuwar Ƙungiya

Tsohon Gwamnan Jihar Kano Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya sanar da ficewarsa daga babar jam’iyyar awada, PDP tare da ɗumbin magoya bayansa.

Gwamnan ya sanar da ficewar ta sa ne a wurin wani taron masu ruwa da tsaki na kafa wata sabuwar ƙungiyar masu kishin ƙasa mai suna “The National Movement” da ya gudana a babban ɗakin taro na “National Conference Center” da ke birnin tarayya Abuja.

Kakaki Network ta ruwaito cewa daga majiyarta ta Nigerian News Hausa da ta wallafa a shafinta cewa, Ƙungiyar ta ƙunshi manyan jiga-jigan ƴan siyasa da ƴan kasuwa da kuma ƙungiyoyin fararen hula.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram