An Naɗa Sabon Mataimakin Gwamna A Zamfara Daga APC Bayan Tsige Mahdi Aliyu Na PDP

Yan majalisar dokokin jahar Zamfara sun amince da naɗin Sanata Hassan Nasiha a matsayin sabon mataimakin gwamnan jahar jim kaɗan bayan tsige mataimakin gwamnan Mahdi Aliyu Gusau.

Sanata Hassan Nasiha wanda shine ɗan majalisar dattawa mai wakiltar Zamfara ta tsakiya a majalisar Dattawa ta Najeriya.

KARANTA WANNAN LABARIN: Da Ɗumi-Ɗumi: Ƴan Majalisar Dokokin Jahar Zamfara Sun Tsige Mataimakin Gwamnan Jahar Mahdi Aliyu

An tabbatar masa da zama mataimakin gwamnan ne ba tare da wasu tambayoyi ba daga ƴan majalisar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram