Takarar Shugaban ‘Kasa: Atiku Ya Ce A Shirye Ya Ke Matasa Su Fito A Kara A Gani

Tsohon Mataimakin Shugaban ‘Kasar Najeriya, Atiku Abubakar ya ce a shirye ya ke ya tsaya takarar Shugabancin ‘Kasar a kakar zabe mai zuwa ta 2023.

Atiku ya bayyana haka ne ga manema labarai Jim kadan bayan ganawarsa da tsohon Shugaban ‘Kasar ta Najeriya, Olusegun Obasanjo a ziyarar da ya kai domin neman goyon bayansa game da tsayawarsa takarar Shugabancin’Kasar.

KARANTA WANNAN LABARIN: Zan Samar wa Ƴan Najeriya Aikin yi, Ilmi Da Cigaba – Inji Tinubu

An tambayi Atiku cewa amma ba ya ganin shi yansu ya kwana biyu kuma ga matasa na ta fafutukar a sakar masu ragamar jagorancin kasar? Sai ya ce to ai magana ce ta siyasa don haka matasan su fito a gwada mana a gani.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram