Buhari Ya Yi Wa Ministan sa Keyamo Ta’aziyyar Mutuwar Mahaifin sa

Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya Mika Ta’aziyyar sa ga Ƙaramin Ministan Ƙwadago da Samar da Ayyukan yi Festus Keyamo SAN kan mutuwar Mahaifin sa.

Ta’aziyyar Buhari na ƙunshi a cikin wata sanarwa da Babban Mai Taimaka Masa akan Kafafen Yaɗa Labaru Garba Shehu ya fitar a ranar Lahadi.

Shugaba Buhari yayi ta’aziyya ga iyalan Keyamo, Abokai da Al’ummar Effurun dake Karamar Hukumar Uvwie ta Jahar Delta a makoki sa, wanda ya kasance Shugaba mai daraja, mai Son ɗiyan sa,da ya koyar dasu yanda zasu yi Shugabanci.

A matsayin na Uba dake girmama kowa, ba tare da nuna bambancin wani abu ba, Shugaban Ƙasa ya yi amanna cewa Pa Keyamo ya kasnace Mai son Cigaban Najeriya, inda ya shafe rayuwar sa a Kaduna da Ilaro ta Jahar Ogun, kafin komawa Ughelli.

Shugaban Ƙasa yayi kira ga iyalan Keyamo dasu yi koyi da kyawawan ɗabi’un sa a matsayin sa na Uba kuma Kaka.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram