TA FARU TA ƘARE: Minista Malami Yace Bazai Ajiye Muƙamin sa Ba

Antoni-Janar na Ƙasa Abubakar Malami kuma Ministan Shari’a a ranar Alhamis yace bazai ajiye muƙamin sa ba.

Malami yace sai yaga ƙarshen wa’adin mulkin sa a watan Mayu na Shekarar 2023.

Malami ya bayyana haka, a lokacin da yake bada jawabin buɗe wa a wani taro, da Ƙungiyar Ma’aikatan Shari’a suka shirya.

“Mutane da dama da suka dogara ga jin bayanai na Ƙarya, suna cewa Malami ya ajiye muƙamin sa a Matsayin Antoni-Janar, kuma Ministan Shari’a, ana ganin sa a ofishin sa yana gudanar da aikace-aikace, ciki harda halartar taron Majalisar Zartaswa ta Ƙasa a jiya, kuma yanzu yana buɗe taro a matsayin Antoni-Janar na Kasa.

“Akwai ƙarshen komai. Wa’adina na Mulki har yanzu bai ƙare ba. Ina fatan inyi kyakkyawan ƙarshe,” inji shi.

Jita-jita na cigaba da yawo cewa Malami zaiyi takarar Kujerar Gwamnan Jahar Kebbi a Shekarar 2023, amma ɗan Shekaru 54 bai bayyana ra’ayin sa ba akan haka.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram