Yajin Aikin ASUU: Jami’ar Bayero ta Umarci Ɗalibai Dasu Bar Makarantar

Jami’ar BUK, ta umurci dukkanin daliban da ke zaune a harabar jami’a guda biyu da su bar dakunan kwanan dalibai da daukacin harabar jami’ar a ranar 20 ga watan Maris ko kuma kafin ranar 20 ga watan Maris.

Jami’ar ta kuma dakatar da shirin ayyukan ta a harabar da aka fara tun da farko har sai an dawo da cikakken ayyukan ilimi.

Wata sanarwa da sakataren yada labarai na jami’ar Bala Abdullahi ya fitar a madadin magatakardar jami’ar, ta bayyana cewa matakin da hukumar ta dauka ya biyo bayan tsawaita yajin aikin gargadi da kungiyar malaman jami’oi ta ASUU ta yi na yajin aikin watanni biyu.

Sannan sanarwar ta kara da cewa “Daga ranar da aka ce hukumar za ta dakatar da bayar da dukkan taimakon na ayyukan ta ga dakunan kwanan dalibai.”

Sanarwar ta ci gaba da cewa an dauki matakan ne don “kare duk wani laifin da ba’a zata ba da kuma sakamakon da zai biyo baya.”

A ranar Alhamis din da ta gabata ne Hukumar Gudanarwar Jami’ar Ibadan (UI), ta rufe cibiyar, inda ta umarci dukkan daliban da su fice daga dakin kwanan daliban da ke cikin makarantar ba tare da bata lokaci ba.

Idan dai ba’a manta ba jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa a wa’adin farko na yajin aikin da kungiyar ta ASUU ta tafi ya haifar da zanga-zanga a sassa daban daban na kasar inda daliban suka nuna rashin amincewar su kan yajin aikin da kungiyar ta ASUU ta keyi.

Kazalika daliban da suka gudanar da zanga-zangar sunyi zargin gazawar ministan ilimi wajen kasa cimma matsaya tsakanin sa da kungiyar ta malam jami’oi ASUU inda wasu daga cikin kungiyoyin dalibai suka bukaci ministan da yayi murabus daga mukamin sa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram