Mai martaba sarkin Katsina Alhaji Abudulmumini Kabir Usman ya yi kira ga malaman addini da su haɗa kansu domin a samu zaman lafiya da magance sauran matsalolin da ke adda bar jahar.
Sarkin ya yi wannan magana ne a wajen taron ganawa da malaman da ofishin mai ba Gwamna Masari shawara akan sha’anin tsaro, Ibrahim Katsina ya shirya domin shawo kan matsalar tsaro da ke adda bar jahar.
Kalli Sarki a cikin wannan hoton bidiyon da ke ƙasa.
Sarkin ya ci gaba da cewa akwai buƙatar malamai su haɗa kansu da kuma yin abu tsakaninsu da Allah ba don ace wane yana da ilimi ba.