Filato: Ƴan Bindiga Sun Kai Hari A Sabon Ginannun Gidajen Ƴan Gudun Hijira, Sun Kashe Mutum 2

Ƴan bindiga sun kashe ƴan gudun hijira guda 2 a Ƙaramar Hukumar Barki Ladi ta Jahar Filato.

An gano cewa wanda lamarin ya shafa, wanda suka yi gudun hijira daga yankunan su a ƙauyen Ratis na Ƙaramar Hukumar, sun dawo ga yankunan su, sun sake gina gidajen da aka lalata, a lokacin da ƴan bindiga suka kai hari.

Shugaban Ƙungiyar Matasan Berom Dalyop Mwantiri ya tabbatar da kisan ga Jaridar PUNCH a Jos a ranar Alhamis.

A cewar sa, sun kuma jikkata wasu mutane 3 a lokacin kai harin.

Shugaban Matasan yace, “an sake samun wani mummunan lamari a ƙauyen Rantis, gundumar Gashish ta Ƙaramar Hukumar Barkin Ladi ta Jahar Filato, inda suka kai hari ga Ƴan Gudun Hijira da misalin ƙarfe 3:30 na ranar 6 ga watan Afrilu na shekarar 2022. A dalilin haka, an tabbatar mutane sun mutu, 3 sun jikkata.

Mai Magana da Yawun Rundunar Ƴan Sandan Jahar Ubah Ogaba ba’a same shi a waya ba a lokacin da aka kira shi domin jin tabbaci.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram