Hisbah ta Ƙwace Kwalabanin Giya 1,426 a Jigawa

Hukumar Hisbah a Jigawa ta ƙwace Kwalabanin Giya 1,426 a Ƙananan Hukumomi guda biyu na Jahar.

Kwamandan Hisbah na Jaha Ibrahim Ɗahiru, ya bayyana haka ga Kamfanin Dillancin Labaru na Ƙasa a Dutse, Babban Birnin Jahar a ranar Alhamis.

Ɗahiru ya bayyana cewar sun kuma ƙwace Jarka mai lita 25 na giyar Hausa Burkutu.

Ya bayyana cewar an ƙwace giyar a lokacin da Jami’an Hisbah suka kai samame a Otal, da Mashaya a Ƙananan Hukumomi guda biyu.

Kwamandan ya ƙara dacewa, mutane 15 da ake zargi da suka haɗa da mata, an kama su a lokacin kai farmakin.

A cewar sa, Kwalabanin Giya 177, da Jarka 25 na Burkutu, da mutane 14 a ranar 3 ga watan Afrilu, a Ƙaramar Hukumar Gumel.

Yace, ” Hisbah ta kama mutane 3 a Ƙaramar Hukumar Gumel a wani Otal na Awala, Dake kan hanyar Gujungu, da Sabuwar Sahara a bayan Sakatariyar Ƙaramar Hukumar da Gidan Mama mai Burkutu.

“A wannan kai harin, mun kama mutane 14, da suka haɗa da wadda ke saida Burkutu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram