Majalisar Wakilai Ta Umarci NAHCON Da Ta Dakatar Da Shirin Adashin Gata Na Hajji

Majalisar Wakilai ta yanke hukuncin baiwa Hukumar Hajji ta Ƙasa, NAHCON umarnin dakatar da shirin Adashin Gata na Hajji, wanda a ka fi sani da Hajj Savings Scheme, HSS.

Wannan yazo ne bisa wani ƙuduri da ɗan majalisa daga Jihar Katsina, Aminu Ashiru Mani ya miƙa, kan buƙatar a gaggauta bincikar shirin.

Dan majalisar ya ce an ƙirƙiro da shirin ne a 2006 domin maniyyata su samu damar yin adashin gata don zuwa aikin Hajji.

Mani ya ƙara da cewa, a cikin shekaru 2 na ƙaddamar da shirin, bisa haɗin gwiwa da bankin Jaiz domin taimaka wa maniyyata su tara kuɗin zuwa aikin Hajji, yawan kwastomomin bankin ya karu da 4,000 inda kuma tuni a ka tara Naira Biliyan 1.

Ya nuna damuwa kan zargin rashin gaskiya da amana a shirin na HSS.

“Idan a ka bar wannan haka, to zai haifar da badaƙalar kuɗaɗe a tsarin da kuma rashin bin doka,”

A nashi ɓangaren, Mataimakin Kakakin Majalisar, Ahmed Wase ya yi bayanin cewa shekaru biyu kenan maniyyata na zuba kuɗi a asusun adashin gatan amma ba su samu zuwa aikin Hajjin ba sabo da korona.

Wase ya zargi NAHCON da karya doka da duma hannu a cikin kuɗaɗen.

Da ga bisani sai a ka umarci kwamitin harkokin alhazai domin ya gudanar da bincike a kan shirin Adashin Gata na Hajji.

Hakazalika majalisar ta umarci kwamitin da ya sake yin nazari a kan ɗaukacin yarjejeniyar da NAHCON ta kulla da Jaiz , sannan ya mika wa majalisar rahoto a cikin makonni biyu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram