Yanzu-yanzu: Adamu, Kyari Sun Yi Murabus Daga Majalisar Dattawa

Yanzu-yanzu: Adamu, Kyari Sun Yi Murabus Daga Majalisar Dattawa

Shugaban jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Adamu a ranar Talata ya yi murabus daga mukaminsa na sanata a majalisar dattawa.

Shi ma Sanata Abubakar Kyari mai wakiltar Borno ta Arewa ya yi murabus daga Majalisar ta Dattawa.

Adamu da Kyari, a wasu wasiku daban-daban da shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan ya karanta, sun ce matakin nasu ya zama wajibi ne biyo bayan fitowar su a matsayin shugaban jam’iyyar APC na kasa da mataimakinsa na kasa a yankin (Arewa).

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram