Rundunar ‘yan sanda a jihar Ogun ta kama wani matashi dan shekara 30 mai suna Ajibola Akindele da laifin yiwa wata yarinya ‘yar shekara 20 fyade a cikin wani coci dake Abeokuta babban birnin jihar.
An kama wanda ake zargin ne biyo bayan rahoton da mahaifiyar yarinyar ta kai hedikwatar ‘yan sanda ta Lafenwa da ke Abeokuta.
Matar ta shaida wa ‘yan sanda cewa lamarin ya faru ne a lokacin da ta aika ‘yarta tare da wanda ake zargin domin yin ado a wani coci da ke unguwar Ita Oshin na garin Abeokuta.
A cewarta, a lokacin da suka isa harabar cocin, sun hadu da wasu mata da suka zo share cocin a shirye-shiryen gudanar da ibadar ranar Lahadi.
Mahaifiyar ta ce “matan suna fita bayan sun share cocin, wanda ake zargin ya yi amfani da damar kasancewa shi kaɗai tare da wance yayi yimata fyaden a cikin cocin.”
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Abimbola Oyeyemi a ranar Alhamis, ya shaida wa manema labarai a Abeokuta cewa, biyo bayan rahoton, DPO na Lafenwa, CSP Kayode Shadrach, ya yi karin bayani ga jami’an da suka gudanar da bincike domin bin diddigin wanda ake zargin.
Ya ce da sauri jami’an ‘yan sandan suka shiga wurin da lamarin ya faru kuma nan take suka kama wanda ake zargin wanda “tun daga nan ya amsa laifinsa.”
Oyeyemi ya ce kwamishinan ‘yan sanda, Lanre Bankole, ya bayar da umarnin mika wanda ake zargin cikin gaggawa sashin yaki da fataucin bil’adama da cin zarafin yara na sashen binciken laifuka da leken asiri na jihar domin ci gaba da bincike tare da gurfanar da shi a gaban kotu.