Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Ruwan Wutan Da Jirgin Yaƙin NAF Ya Yi Kan Ƙananan Yara

Sakataren gwamnatin jihar Neja, Ibrahim Matane, ya tabbatar da kisan wasu yara shida da wani jirgin yakin sojin Saman Kasar Nan NAF ya yi a jihar.

Matane ya ce ana gudanar da bincike kan lamarin wanda ya faru a makon jiya, inda ya ce an kashe yaran ne a wani samame da aka kai wa ‘yan ta’addan.

Lamarin ya faru ne a unguwar Kurebe da ke karamar hukumar Shiroro ta jihar Neja.

Da aka tambaye shi ko wani jirgin yakin NAF ya kashe yara 6?, Matane ya amsa da cewa, “Eh, hakan ya faru, gwamnati na duba lamarin kuma ana ci gaba da bincike don gano me ya faru.”

A cewar shugaban gamayyar kungiyoyin Shiroro, Salis Sambo, wanda ya zanta da wakilin Jaridar Daily Trust, ya ce yaran sun mutu ne a lokacin da jiragen yakin suka yi kokarin Saka bam ga wasu ‘yan ta’adda da suka shiga cikin al’umma domin tsira da rayukansu.

Ya ce yaran da abin ya shafa na dawowa ne daga rafi da suka je diban ruwa, inda ya ce hudu daga cikin yaran ‘yan gida daya ne.

“’Yan ta’addan ne suke kaiwa hari. A wancan makon an kai hare-hare ta sama kusan hudu a Shiroro kuma an kashe ‘yan ta’adda da dama. ‘Yan ta’addan sun shiga cikin al’umma domin samun mafaka inda aka harba bama-baman, lamarin ya shafi yaran. Ba da gangan ba ne, ”in ji shi.

Sambo ya ce wani mutum ya rasa ‘ya’yansa mata biyu da jikoki biyu a yayin lamarin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram