Zaɓen 2023: Sakataren Gwamnati, da Kwamishinoni 11 Sun Yi Murabus A Sokoto

Akalla kwamishinoni 11 ne suka yi murabus daga mukamansu a majalisar Kwamishinin Gwamna Aminu Tambuwal na jihar Sokoto.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa kwamishinonin sun hada da na ma’aikatun Fili da gidaje, Aminu Bala Bodinga,; Matasa da Wasanni, Bashir Gorau; Kudi, Abdussamad Dasuki; harkokin tsaro da hukumomin su, Garba Moyi da Kwamishinan Ma’aikatar harkokin addini na jihar ta Sokoto, Abdullahi Maigwandu.

Sauran sun hada da kwamishinonin ayyuka, Salihu Maidaji; Ma’adanai, Abubakar Maikudi; Albarkatun Ruwa, Shu’aibu Gwanda Gobir; Muhalli, Sagir Bafarawa da karamar hukumar, Manir Dan’iya wanda har yanzu mataimakin gwamnan jihar ne da kuma kwamishinan kasuwanci, Bashir Gidado.
Majiyar Jaridar Dimokuradiyya ta ci gaba da cewa Sakataren Gwamnatin Jihar Sakkwato Sa’idu Umar Ubandoma da Shugaban Ma’aikatan Gwamnan Jihar Mukhtar Umar Magori su ma sun yi murabus.

Rahotanni sun kuma bayyana cewa Tambuwal ya amince da murabus din nasu.

A cikin makonni biyun da suka gabata, kusan kwamishinoni 50 ne suka yi murabus a jihohi daban-daban Dake fadin kasar nansaboda zaben shekarar 2023.

Sashe na 84 (12) na dokar zabe ta shekarar 2022 (kamar yadda aka gyara) ya nuna cewa, Babu Wani Dan Takarar da zai tsaya takarar kujerar siyasa ta zabe a zaben shekarar 2023, Kuma Yana rike da mukamin siyasa na nadi.

Bisa jadawalin zaben da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta fitar, jam’iyyun siyasa na da damar gabatar da sunayen Yan takaransu a babban zaben kasarnan zuwa ranar 3 ga watan Yunin shekarar 2022.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram