Jam’iyyar PDP Ta Tantance Ƴan Takarar Sanatoci Da Ƴan Majalisu A Lagos

Jam’iyyar PDP reshen Jahar Lagos a ranar Laraba ta tantance Ƴan Takarar Sanatoci, da Ƴan Majalisun Tarayya dana Jaha.

Tantance Ƴan Takarar Sanatoci Ƴan Majalisun Wakilai ya wakana a otel na Regency Dake GRA Ikeja a Lagos, a yayinda Ƴan Majalisu na Jaha ya wakana a otel na White House GRA a Ikeja, Lagos.

A cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labaru Hakeem Amode ya fitar mai kwanan watan 19 ga watan Afrilu na Shekarar 2022, ya nuna yadda Ƴan Takarar Sanatoci ake kira dasu biya Naira dubu 350,000 inda Ƴan Majalisun Tarayya ake karɓi Naira 200,000 daga hannun su.

Ƴan Majalisun Jaha ana karɓar Naira dubu 50,000, inda za’a karɓi Naira Dubu 500,000 daga Masu Takarar Gwamna, kuɗin Sashen Mulki.

Ƴan Takarar wanda suka iso wurin da misalin ƙarfe 9 na safe, an buƙace su dasu biya shaidar biyan kuɗin inda suka yi.

Duk da irin gargaɗin da Mataimakin Shugaban Jam’iyyar na Kasa Chief Olabode George Yayi akan irin waɗannan kuɗin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram