An Yi Sallar Idi A Jahohin Sokoto Da Kebbi A Yau Lahadi

Wasu al’ummar Musulmi a jahohin Sokoto da Kebbi da ke Arewacin Najeriya sun gurdanar da Sallar Idin ƙaramar sallah a yau Lahadi.

BBC Hausa ta ce a jihar Sokoto, Sheikh Musa Lukwa ne ya jagoranci Idi da mabiyansa a ranar Lahadin.

Hakazalika a garin Jega na jihar Kebbi sun gudanar da Sallarsu da Idi.

Mai alfarma sarkin musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar ya ayyana ranar Litinin a matsayin ranar Sallah bayan kasa ganin watan Shawwal a ranar Asabar.

Samun irin wannan saɓani ba sabon babu ba ne a Najeriya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram