Minista Malami Ya Ƙaryata Labarin Da Aka Yaɗa Cewa Ya Raba Motoci

Ministan Shari’a kuma Antoni-Janar na Ƙasa, Abubakar Malami ya musanta labaran da su ka yaɗu a jiya na cewa ya raba motoci na-gani-na-faɗa ga magoya bayan sa.

Malami ya ƙaryata labarin ne a yayin wata ganawa da manema labarai jiya Talata a Birnin Kebbi.

A cewar sa” a kwanakin nan ina shan sharri iri-iri, ta sama, ta ƙasa ta tsakiya, wasu a nan cikin gida wasu kuma daga ƙasashen waje. Har da sahrrin cewa wai na raba motoci ga masu tsada ga ƴan jam’iyar APC.

“A matsayina na mutum mai abokai da dama, ko ni, ko su, babu wanda ya raba wata mota ga kowanne wakilin jami’ya a faɗin jihar nan,” in ji shi.

Malami ya kuma suffanta kabarin a matsayin yarfe da kuma sharri.

Ya kuma yi bayanin cewa shi dai ya san ya gana da shugabannin APC a jihar sakamakon amsa kira da ya yi na al’ummar Kebbi kan ya fito takarar gwamna.

Ya kara da cewa, bayan ganawar, babu wani shugaba ko wakili na jam’iya da a ka baiwa kyautar mota.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram