Shugaban kwamitin kasafin kudi na Majalisar Dattawa, Sanata Barau I Jibrin na Kano ta Arewa ya janye kudirinsa na tsayawa takarar gwamna tare da sayen fom din takarar Sanata.
Da wannan ci gaba Barau zai kalubalanci Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, wanda masu ruwa da tsakin jam’iyyar suka amince masa da ya nemi wannan kujera.
Barau, daya daga cikin jiga-jigan ‘yan takarar gwamna a jihar Kano, ya janye aniyarsa ta sa’o’i 24 bayan Ganduje ya nada mataimakinsa a matsayin dan takarar gwamna a jam’iyyar.
Majiyoyi sun ce dan majalisar wanda daya ne daga cikin shugabannin kungiyar G-7 da ta balle a jam’iyyar APC ta Kano, shugabannin jam’iyyar sun yi nasara a kan ya janye aniyarsa ta tsayawa takarar gwamna ya koma majalisar dattawa.
Dan majalisar, a wata hira ta wayar tarho ya tabbatar da cewa ya dauki fom din komawa kungiyar ta Red Chamber.
Idan za iya tunawa a jiyane masu ruwa da tsakai suka baiwa gwamnan kano Abdullahi Ganduje damar tsayawa takarar Sanatan kano ta Arewa.
Sai dai a iya cewa wannan matakin da gwamnan kano ya samu baiyiwa Barau Jibrin dadi ba inda ya yanke shawarar a jiye ta karar sa ta gwamna ya nemi fom din karar sanata.