Rashin Doka Ce Tsantsa Sare Kan Ɗan Majalisa A Najeriya – Shehu Sani

Sare kan Ɗan Majalisa na Anambra Ikechukwu Okoye an bayyana shi a matsayin rashin bin Doka tsantsa dake cigaba da yaɗuwa a Najeriya.

An gano kan Okoye ba tare da gangar jikin sa ba a ranar Asabar a Nnobi na Ƙaramar Hukumar Idemili ta Jahar Anambra, kwanaki bayan sace shi.

Dayake maida jawabi akan wannan mummunan lamari, Shehu Sani ya bayyana hakan a matsayin abun damuwa, kuma abun Allah wadai.

A cewar sa, irin wannan mummunan kisa, ya nuna cewa akwai rashin bin Doka tsantsa dake cigaba da yaɗuwa a dukkanin sassa na Najeriya.

Tsohon Sanatan yayi wannan jawabin a shafin sa na Twita, “Sare kan Ɗan Majalisa okechukwu Okoye da ƴan ta’adda suka yi abin Allah wadai ne.

“Kuma hakan ya nuna cewa rashin Doka yana cigaba da fantsama a dukkanin sassan Ƙasar”.

Haka zalika, Gwamnan Jahar Anambra Farfesa Charles Soludo ya sanya tukuicin Naira Miliyan 10 ga duk wanda ya gano makasan Okoye.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram