Tarihi Ne Zai Maimaita Kanshi, Idan Tinubu Ya Zama Shugaban Ƙasa — Tanko Yakasai
Wani Dattijo Alhaji Tanko Yakasai ya yaba kan samun nasarar Bola Tinubu a matsayin Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa na Jam’iyyar APC.
A cikin sanarwar daya fitar a ranar Alhamis, Yakasai yace Tarihi zai maimai ta kanshi Idan har Tinubu ya zama Shugaban Ƙasar Najeriya.
Dattijon yace idan Tinubu ya zama Shugaban Ƙasa ya nuna “ɓallewa ne daga masu nuna Mallakin Najeriya.
Yace, “Zaɓen Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a matsayin Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa a APC, Cigaban Siyasa ne a Ƙasar. Wannan zai sanya mu shiga siyasa gadan-gadan, da cigaba.
“A lokacin da Asiwaju, ya zama Shugaban Ƙasar Najeriya a Zaɓen Shugaban Ƙasa, Tarihi zai maimaita kansa a tarihin cigaban Siyasa.