Yanzu-Yanzu: Super Eagles Ta Doke Saliyo Neman Gurbin Zuwa Gasar Cin Kofin AFCON
Tawagar Super Eagles ta Najeriya ta lallasa kasar Saliyo da ci 2-1 a wasan farko na neman tikitin shiga gasar cin kofin Afrika (AFCON) da suka fafata a filin wasa na Mashood Abiola ranar Alhamis.
Jonathan Morsay ne ya fara cin kwallo a minti na 11 da fara wasa, sai dai kuma dan wasan Everton Alex Iwobi ya yi gaggawar ramawa Najeriya kwallo a minti na 16 da fara wasa.
Victor Osimhen ne ya kara kwallon daga bugun daga kai sai mai tsaron gida da Moses Simon ya yi a minti na 41 da fara tamaula, lamarin da ya sa ‘yan Najeriyar suka samu dukkan maki uku.
Da wannan nasarar Najeriya ta zama ta biyu a rukunin A da maki uku a wasa daya.
Guinea-Bissau ce ta daya a kan teburi, Najeriya, ta nada ragowar kwallaye 4 a raga bayan ta doke Sao Tome and Principe da ci 5-1 a karawarsu.