Tinubu Da Yahaya Bello, Sun Yi Ganawar A yau Juma’a

Daga Wakiliyar mu Amira Salisu Batsari

Dan Takarar Shugaban Ƙasa a Jam’iyyar APC Kuma Tsohon Gwamnan Jahar Lagos, Asiwaju Bola Tinubu na ganawar sirri tare da Gwamnan Jahar Kogi Yahaya Bello, akan abinda masana siyasa suka bayyana cewa, wani yunƙuri na yin sasanci da ƴan Takarar APC da suka nemi takara

Tinubu yayi ganawar Sirrin a yau Juma’a, bayan ya samu rakiyar Gwamnan Jahar Lagos, Babajide Sanwa-Olu, da Gwamnan Jahar Zamfara Bello Matawalle, da kuma Gwamnan Jahar Kano, Abdullahi Umar Ganduje.

Tsohon Gwamnan Jahar Edo, da Tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na kasa, Adams Oshiomhole, na daga cikin ƴan tawagar.

Amma babu tabbacin idan samun Abokin Takarar Tinubu na daga cikin abinda za’a tattauna.

Jaridar PUNCH ta lura cewa, zasu yiwa Manema labaru jawabi akan dalilin taron sirrin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram