Babu Abinda Mulkin Jam’iyyar APC Ya Kawo A Najeriya Sai Talauta Jama’a – Shema

Tsohon gwamnan jahar Katsina a ƙarƙashin jam’iyyar PDP Barista Ibrahim Shema ya ce babu abinda mulkin APC ya haifar a Najeriya sai talauta jama’a

Focus News Hausa ta ruwaito cewa, tsohon gwamnan ya ce mutane ma su sana’o’i jarinsu ya wargaje, yunwa da fatara sun dami al’umma a cikin ƙasar.

Shema ya ci gaba da cewa, matsalar rashin tsaro ta zama ta addabi ko wane ɓangare a Najeriya.

Sai dai ya ƙara da cewa Allah ba ya kuskure don haka Allah ya yi haka ne domin al’umma su fahimci wacece APC da mutanen cikinta.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram