An bukaci maniyyata aikin hajjin jihar Kaduna da su bi ka’idojin addinin Musulunci a yayin da suke gudanar da aikin hajji.
Babban Sakataren Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna, Yakubu Arrigasiyyu ne ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi ga maniyyatan da suke aikin tantancewa a sansanin Alhazai da ke Mando, Kaduna.
A cewarsa, yana da kyau su nemi ilimin da ya dace na dukkan ayyukan hajji domin su samu nasarar gudanar da aikin hajjin.
“Kudin aikin hajjin bana yana kan babban matsayi, ba zai dace ku hadu a birni mai alfarma ba kuma ba ku yi aikin hajji da kyau ba. Yana da mahimmanci ku hadu da jami’an da suke da gogewa da ilimi domin su jagorance ku kan dukkan ayyukan da ake sa ran ku yi shi ,” inji shi.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar, Sani Anchau ya ce kimanin mahajjata 2491 ne za a yi jigilar su zuwa kasa mai tsarki ta hanyar kamfanonin jiragen sama na Azman.
A cewarsa, mahajjatan da za a yi jigilarsu ta jirgin sama, za a fito da su ne daga kananan hukumomi daban-daban.
“Saboda annobar korona, ana sa ran maniyyata za su sami allurai 3 na allurar rigakafin corona wanda shi ne babban sharudda na bayar da biza. Don haka ne kawai wadanda aka shirya bizarsu a wani lokaci, ba tare da la’akari da kananan hukumominsu ba, za a tantance su a kai su kasa mai tsarki,” inji shi.
Amma Anchau ya ba da tabbacin cewa, duk biza za su kasance a shirye kuma za su kasance a cikin lokacin da ake sa ran jirgin zai tashi.
‘Yan jarida sun lura cewa sansanin Hajjin da ba a yi amfani da shi ba tsawon shekaru biyu saboda annobar korona, an gyara shi tare da sanya muhallin zaman lafiya ga maniyyata su zauna kafin tashin jirgi.