Za’a Mance Kiristoci Ne Idan Aka Yi Takarar Musulmi Da Musulmi – Inji Wani Bishop

Janar-Sufirtanda na God Mission International Bishop Paul Nwachukwu yace takarar Musulmi da Musulmi a zaɓen Shugaban Ƙasa na Shekarar 2023, kiristoci bazasu taɓa amince wa dashi ba.

Nwachukwu yace manyan Jam’iyyu guda biyu da suka zaɓi musulmi a matsayin Ɗan Takarar su tuna cewa Najeriya ƙasa ce mai Mabambantan ra’ayoyi, da addini.

Yace zaɓen musulmai a matsayin abokanan takarar su, zai haifar da mance kiristoci kenan.

A cikin wata sanarwa mai taken “ina son ƴan Siyasa su tuna cewa Najeriya ƙasa ce mai Mabambantan ra’ayoyi, kuma a wurin ɗaukar abokanan takarar su, baza’a yarda su ƙara ɗaukar wani musulmi ba.

“Najeriya ta kowa da kowa ne, kuma kowane ɓangare da Addini yana da mahimmanci. Zaɓen musulmi a matsayin abokin Takara, zai haifar da mance kiristoci,” Inji Nwachukwu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram