Yanzu-Yanzu: APC Lashe Rumfar Farko Da Aka Bayyana Sakamakonta A Zaɓen Ekiti
Jam’iyyar APC mai mulki ta samu nasarar farko a zaben gwamna da ke gudana a jihar Ekiti.
A rumfar zabe ta 10, ward 10, Afao/Kajola, Abiodun Oyebanji, dan takarar gwamna na APC ya samu kuri’u 20 inda ya dokr Bisi Kolawole na jam’iyyar PDP, wanda ya samu kuri’u biyu.
Babu wani dan takara da ya samu kuri’a daya a rumfar zaben.
Wakilin cibiyar kirkire-kirkire da ci gaban aikin jarida (CJID) ya ruwaito cewa an fara tantance masu kada kuri’a ne da karfe 8:30 a wurin kada kuri’ar