Ɗan Takarar Gwamnan Rivers A ADC, Ya Ɗauki Jaruma Tonto Dikeh Abokiyar Takarar shi
Ɗan Takarar Gwamnan Jahar Rivers a Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ya ɗauki Tonto Dikeh ƴar wasan kwaikwayo kuma Jaruma Tonto.
Jarumar ta sanar da hakan a shafin ta na Instagram a safiyar ranar Juma’a da safe.
“Na gode ma, Me Tonte Ibraye (@tonteibraye), Ɗan Takarar Gwamnan Jahar Rivers a ADC daya ɗauke Ni a matsayin abokiyar takarar shi.
“Yanzu mun fara tattaunawa akan yadda zamu tunkari yadda za’a samar da tsaro, da ɓullo da tsare-tsare ga Matasa, da shigo da mata a harkokin Gwamnati, bada tallafi ga kasuwanci, inganta Masarautun gargajiya, tare da samar da cigaba ga Al’ummar Jahar Rivers.
“Ina jindaɗi, sannan
mun fara tattaunawa akan yadda zamu tunkari yadda za’a samar da tsaro, da ɓullo da tsare-tsare ga Matasa, da shigo da mata a harkokin Gwamnati, bada tallafi ga kasuwanci, inganta Masarautun gargajiya, tare da samar da cigaba ga Al’ummar Jahar Rivers.
“Ina jindaɗi, sannan ina jinjina dana zama ɗaya daga cikin shirin ceto Jahar Rivers #RiversRescueMission2023. Kuje ku samu Katin Zaɓen ku, sai kum zo ku haɗa damu.Kune makomar gobe, kuma itace yanzu! TontoTonto2023,” ta rubuta