An Ga Watan Dhul Hijjah A Saudiyya, Za’ayi Babbar Sallah Ranar Asabar

 

An ga jinjirin watan Dhul Hijjah a kasar Saudiya inda Gobe Alhamis ya zama daya ga wata.

Hakan yanuna cewa, Za a gudanar da hawan Arfa kenan a ranar Juma’a 8 ga watan Yulin shekarar 2022, wanda kuma Ranar Sallah zai kama Asabar 9 ga watan Yuli.

Hukumomin kasar ne huka sanar da hakan a shafin suna facebook mai suna Harafaini Sharafaini.

Idan za’a iya tunawa Jaridar Dimokuradiyya ta ruwaito cewa, hukumomin saudiyya a jiya sun bada sanarwar fara duba jinjirin watan na Dhul Hijjah.

Sai dai a gefe guda har yanzu a Najeriya a na dakon sanarwar ganin watan na Dhul Hijjah da ga fadar mai Alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar Na Uku

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram