Wani matashi ya je kauyen Kanoke cikin karamar hukumar Kiyawa a Jihar Jigawa.
ya yaye rufin Masallaci bisa alkawarin zai gina musu sabo.
To saidai bayan faruwar haka daga baya aka gano cewa dan damfara ne, ya kwashe rufin da kofofi da tagogin masallacin ya siyar.
BBC Hausa ta ce, Kakakin ‘yan sandan jihar Jigawa DSP Lawal Shi’isu Adam ya ce sun kama matashin sun kuma gurfanar da shi a gaban kotu.