Babu Kokwanto Tinubu Ne Zai Lashe Ƙuri’un Adamawa Ba Atiku Ba – Shugaban Matasan APC

Shugaban matasan jam’iyyar APC na kasa, Dayo Israel, ya ce dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Bola Tinubu zai doke takwaransa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar a jiharsa ta Adamawa.

Isra’ila ya bukaci mazauna jihar Adamawa da su kada kuri’unsu, su kuma tabbatar da cewa Tinubu ya kayar da Atiku a jiharsa, a zaben watan Fabrairu.

Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake karbar wasu masu sauya sheka daga PDP zuwa APC a jihar Adamawa.

Isra’ila ya ce sauya shekar manuniya ce da ke nuna cewa jam’iyyar APC na kara samun nasara gabanin zaben 2023 kuma za ta yi nasara a watan Fabrairu.

A cewar Isra’ila, jihar za ta taka rawar gani wajen fitowar Tinubu a matsayin shugaban Najeriya a 2023.

Tinubu da Atiku dai na daga cikin ‘yan takarar da ke kan gaba a zaben shugaban kasa na 2023.

Yayin da Tinubu ya fito daga jihar Legas, Atiku kuwa dan jihar Adamawa ne.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram