Zan Mayar Da Jarabawar WAEC Da NECO Kyauta, Zan Ƙarawa JAMB Lokacin Lalacewa – Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa jarrabawar kammala karatun sakandare a Najeriya ta NECO, WAEC, NABTEBE, NBAIS, duk zasu kasance kyauta ne ga dalibai yan kasar.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a yau, yayin da yake bayyana kundin manufofin takararsa ta shugaban ƙasa (Blueprint) idan har yayi nasarar zama shugaban ƙasa a zaben 2023.

Kwankwaso yana taron ƙaddamar da jadawalin kundin manufofin takararsa a babban birnin tarayyar Abuja, inda yace za’a kara wa’adin jarabawar neman gurbin shiga jami’a ta JAMB zuwa shekaru hudu kafin ta daina aiki.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Social media & sharing icons powered by UltimatelySocial
YouTube
YouTube
Instagram